• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta
  • General

Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta

By
'ƴan Bindiga
-
August 29, 2024
Arewa Award

Rundunar Tsaron Najeriya ta ce sojojinta sun kashe ‘ƴan bindiga sama da 1,000 a cikin wannan watan a faɗin Najeriya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Rundunar Tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba, inda a ciki ya bayyana cewa aikace-aikacen sojin yana matuƙar daƙile ayyukan ƙungiyoyin ƴan bindigar.

“Muna sane cewa muna yaƙi ne da maƙiya marasa imani, wanda hakan ya sa dole mu ƙara ƙaimi wajen dakatar da su.”

Ya ce daga shirye-shiryen sojojin, akwai takura ƴan bindigar domin hana su sakat, “sannan sojojin suna bibiyar kwamandojin ƴan ta’addan da yaransu da ma masu taimaka musu.”

Ya ƙara da cewa tuni sun ga bayan wasu manyan kwamandojin ƙungiyoyin a watan “A Arewa ta Gabas an kashe irin Munir Arika da Sani Dilla (AKA Dan Hausawan Jibilarram) da Ameer Modu da Dan Fulani da Fari Fari da Bakoura Araina Chikin da Dungusu da Abu Darda da Abu Rijab.”

Read Also:

  • Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa
  • Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya
  • Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a yankin Arewa maso Yamma sojojin sun ga bayan manyan ƴan bindiga kamar su Kachalla Ɗan Ali Garin Fadama da Kachalla Ɗan Mani Na Inna da Kachalla Basiru Zakariyya da Sani Baka Tsine da Inusa Zangon Kuzi da Ibrahim da Tukur da Kamilu Buzaru da sauransu.

“Sojoji sun samu gagarumar nasara a kan ƴan bindigar, sannan kuma suna ci gaba da ƙara ƙaimi a aikace-aikacen da suke yi a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas domin magance matsalar tsaron da ake fama da su.”

Ya ce jimilla a watan Agusta, sojoji sun kashe ƴan ta’adda 1166, an kama guda 1,096 sannan an tseratar da waɗanda aka kama guda 721.

Haka kuma a cewar sanarwar, ak ƙwato makamai 391, da alburusai 15,234, sannan sun daƙile satar mai da aka ƙiyasta ya kai na Naira biliyan 5.

“Aikace-aikacen sojojin sun sa ƴan bindigar sun ja baya sosai, wanda hakan ya sa suke ta miƙa wuya, musamman a Arewa maso Gabas,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa sojojin za su ƙara matsa lamba a sauran yankunan domin samun irin wannan nasarar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Agusta
  • Edward Buba
Previous articleSojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna
Next articleGwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki
'ƴan Bindiga

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Mamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a Maiduguri

Hadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar Jigawa

Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rasuwar Sarkin Gusau na jihar

akwai yuwuwar katsewar wutar lantarki a Nijeriya saboda bashi – Kamfanonin samar da wuta

Kotu Ta Kori Karar Da APC Ta Shigar Domin Hana Kudaden Kananan Hukumomi

Za a yi ruwan sama da iska mai ƙarfi a sassan Najeriya – NiMET

Dakarun MNJTF sun kashe kwamandan Boko Haram a Tafkin Chadi

Tarihi bazai manta da Buhari ba – Osibanjo

Gwamnatin Najeriya ta ciyo bashin dala miliyan 747

Gwamnan Kano ya naɗa sabon shugaban ma’aikatan fadar Gwamnatin jihar

Ƴanbindiga sun hallaka ƴan banga a jihar Filato

Kotu ta Umarci majalisa ta dawo da Sanata Natasha

Recent Posts

  • Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa
  • Tinubu ya yi karin wa’adin Aiki ga shugaban Custom na Nijeriya
  • Gini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar Maiduguri
  • KACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami’anta
  • Dino Melaye ya koma jam’iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDP

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1507 days 9 hours 19 minutes 44 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1489 days 11 hours 1 minute 9 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Gwamnan Kano ya aikewa Majalisar dokoki sunan wanda zai shugabanci hukumar yaki da cin hanci da rashawaTinubu ya yi karin wa'adin Aiki ga shugaban Custom na NijeriyaGini kan magudanan ruwa ne ya haifar da Ambaliyar MaiduguriKACHMA ta yabawa KAROTA bisa inganta lafiyar Jami'antaDino Melaye ya koma jam'iyyar ADC bayan ficewarsa daga PDPMamakon ruwan sama ya haifar da ambaliya a MaiduguriAn samu raguwar hare-haren Boko Haram da na ƴan bindiga - RibaduHadarin jirgin ruwa yayi sanadin mutuwar mutum 6 a jihar JigawaZanga-zanga ta barke a sansanin ƴan gudun hijra mafi girma da ke Kenyazamu hallaka Da;iban da ke hannun mu matukar baku biya Fansa ba - 'Yan BindigaGwamnan Zamfara ya Amince da Nadin Sabon Sarki GusauAkalla jami'an tsaron jihar Katsina 100 suka mutu a bakin aiki - KwamishinaYadda yan bindiga suka yiwa mutane 38 yankan RagoAmbaliyar ruwa ta lalata gidaje tare da kashe mutane 23 da a birnin YolaFadar shugaban Kasa ta magantu kan zargin da Kwankwaso ya yiwa Tinubu
X whatsapp