• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta
  • General

Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta

By
'ƴan Bindiga
-
August 29, 2024
Arewa Award

Rundunar Tsaron Najeriya ta ce sojojinta sun kashe ‘ƴan bindiga sama da 1,000 a cikin wannan watan a faɗin Najeriya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Rundunar Tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba, inda a ciki ya bayyana cewa aikace-aikacen sojin yana matuƙar daƙile ayyukan ƙungiyoyin ƴan bindigar.

“Muna sane cewa muna yaƙi ne da maƙiya marasa imani, wanda hakan ya sa dole mu ƙara ƙaimi wajen dakatar da su.”

Ya ce daga shirye-shiryen sojojin, akwai takura ƴan bindigar domin hana su sakat, “sannan sojojin suna bibiyar kwamandojin ƴan ta’addan da yaransu da ma masu taimaka musu.”

Ya ƙara da cewa tuni sun ga bayan wasu manyan kwamandojin ƙungiyoyin a watan “A Arewa ta Gabas an kashe irin Munir Arika da Sani Dilla (AKA Dan Hausawan Jibilarram) da Ameer Modu da Dan Fulani da Fari Fari da Bakoura Araina Chikin da Dungusu da Abu Darda da Abu Rijab.”

Read Also:

  • NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas
  • Likitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗi
  • Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a yankin Arewa maso Yamma sojojin sun ga bayan manyan ƴan bindiga kamar su Kachalla Ɗan Ali Garin Fadama da Kachalla Ɗan Mani Na Inna da Kachalla Basiru Zakariyya da Sani Baka Tsine da Inusa Zangon Kuzi da Ibrahim da Tukur da Kamilu Buzaru da sauransu.

“Sojoji sun samu gagarumar nasara a kan ƴan bindigar, sannan kuma suna ci gaba da ƙara ƙaimi a aikace-aikacen da suke yi a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas domin magance matsalar tsaron da ake fama da su.”

Ya ce jimilla a watan Agusta, sojoji sun kashe ƴan ta’adda 1166, an kama guda 1,096 sannan an tseratar da waɗanda aka kama guda 721.

Haka kuma a cewar sanarwar, ak ƙwato makamai 391, da alburusai 15,234, sannan sun daƙile satar mai da aka ƙiyasta ya kai na Naira biliyan 5.

“Aikace-aikacen sojojin sun sa ƴan bindigar sun ja baya sosai, wanda hakan ya sa suke ta miƙa wuya, musamman a Arewa maso Gabas,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa sojojin za su ƙara matsa lamba a sauran yankunan domin samun irin wannan nasarar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Agusta
  • Edward Buba
Previous articleSojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna
Next articleGwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki
'ƴan Bindiga

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas

Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15

Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi

Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Ƙungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a Najeriya

‘Yan sandan Jigawa sun kama Dilolin kwaya a jihar

Kofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPP

Gwamnatin Najeriya ta yi maraba da ɗaure Simon Ekpa a Finland

Atiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin Rivers

An yanke wa ɗan Najeriya Simon Ekpa hukuncin ɗaurin shekara 6 a Finland

Sojoji da DSS sun kashe ƴan bindiga 50 a jihar Neja

ASUU na barazanar shiga yajin aiki a jami’o’in Najeriya

Recent Posts

  • NDLEA ta kama Ba’indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a Legas
  • Likitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗi
  • Kotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15
  • Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin Mauludi
  • Hukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar Ansaru

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1551 days 18 hours 42 minutes 59 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1533 days 20 hours 24 minutes 24 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
NDLEA ta kama Ba'indiye da wasu mutane da ƙwaya ta naira biliyan uku a LegasLikitoci a Najeriya sun janye yajin aikin gargaɗiKotu ta yanke wa kwamandan Ansaru hukunci ɗaurin shekaru 15Gwamnatin Kano ta bayar da hutun bikin MauludiHukumar DSS ta yi holen manyan kwamandojin ƙungiyar AnsaruNUPENG ta cimma matsaya da kamfanin DangoteƘungiyar ƙwadago ta TUC ta yi barazanar shiga yajin aiki a NajeriyaEl-Rufa'i ya shigar da ƙorafi kan zargin ƴansanda da cin zarafi'Yan sandan Jigawa sun kama Dilolin kwaya a jiharKofa ya sanar da ficewarsa da ga NNPPBurkina Faso ta amince da dokar haramta neman maza a faɗin ƙasarAn bayyana jihohin arewacin Najeriya da za su iya fuskantar ambaliya a watan SatumbaGwamnatin Najeriya ta yi maraba da ɗaure Simon Ekpa a FinlandAtiku ya nemi a soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomin RiversAn yanke wa ɗan Najeriya Simon Ekpa hukuncin ɗaurin shekara 6 a Finland
X whatsapp