• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta
  • General

Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta

By
'ƴan Bindiga
-
August 29, 2024
Arewa Award

Rundunar Tsaron Najeriya ta ce sojojinta sun kashe ‘ƴan bindiga sama da 1,000 a cikin wannan watan a faɗin Najeriya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Rundunar Tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba, inda a ciki ya bayyana cewa aikace-aikacen sojin yana matuƙar daƙile ayyukan ƙungiyoyin ƴan bindigar.

“Muna sane cewa muna yaƙi ne da maƙiya marasa imani, wanda hakan ya sa dole mu ƙara ƙaimi wajen dakatar da su.”

Ya ce daga shirye-shiryen sojojin, akwai takura ƴan bindigar domin hana su sakat, “sannan sojojin suna bibiyar kwamandojin ƴan ta’addan da yaransu da ma masu taimaka musu.”

Ya ƙara da cewa tuni sun ga bayan wasu manyan kwamandojin ƙungiyoyin a watan “A Arewa ta Gabas an kashe irin Munir Arika da Sani Dilla (AKA Dan Hausawan Jibilarram) da Ameer Modu da Dan Fulani da Fari Fari da Bakoura Araina Chikin da Dungusu da Abu Darda da Abu Rijab.”

Read Also:

  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a yankin Arewa maso Yamma sojojin sun ga bayan manyan ƴan bindiga kamar su Kachalla Ɗan Ali Garin Fadama da Kachalla Ɗan Mani Na Inna da Kachalla Basiru Zakariyya da Sani Baka Tsine da Inusa Zangon Kuzi da Ibrahim da Tukur da Kamilu Buzaru da sauransu.

“Sojoji sun samu gagarumar nasara a kan ƴan bindigar, sannan kuma suna ci gaba da ƙara ƙaimi a aikace-aikacen da suke yi a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas domin magance matsalar tsaron da ake fama da su.”

Ya ce jimilla a watan Agusta, sojoji sun kashe ƴan ta’adda 1166, an kama guda 1,096 sannan an tseratar da waɗanda aka kama guda 721.

Haka kuma a cewar sanarwar, ak ƙwato makamai 391, da alburusai 15,234, sannan sun daƙile satar mai da aka ƙiyasta ya kai na Naira biliyan 5.

“Aikace-aikacen sojojin sun sa ƴan bindigar sun ja baya sosai, wanda hakan ya sa suke ta miƙa wuya, musamman a Arewa maso Gabas,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa sojojin za su ƙara matsa lamba a sauran yankunan domin samun irin wannan nasarar.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 20 hours 24 minutes 37 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 6 minutes 2 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Agusta
  • Edward Buba
Previous articleSojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna
Next articleGwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki
'ƴan Bindiga

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya

Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC

Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya

A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu

Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Nan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya – Dangote

Sojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a Zamfara

An samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari Mansur

Gwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Jirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga’

Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 ‘yan asalin Kano

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan ta’adda 60 a jihar Borno

Recent Posts

  • DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiya
  • Najeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu – OPEC
  • Tinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyya
  • A aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a Mangu
  • Najeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga Saudiya

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 20 hours 24 minutes 37 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1444 days 22 hours 6 minutes 2 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
DR Congo da Rwanda sun cimma yarjejeniyar zaman lafiyaNajeriya ce kan gaba a yawan fitar da man fetur a Afirka cikin watan Mayu - OPECTinubu zai yi wa ƴan Najeriya jawabi kan ranar dimokuraɗiyyaA aƙalla mutum 20 sun rasa rayukansu a saboda hare-hare a ManguNajeriya na fuskantar tsaiko kan shirinta na karɓar Dala biliyan 5 daga SaudiyaBom ya kashe masu yawon murnar sallah a SakkwatoNan bada jimawa ba za a samu sauyi a ɓangaren man fetur na Najeriya - DangoteSojojin Najeriya sun kashe ƴan ta’adda 10 a ZamfaraAn samu tashin gobara a masaukin alhazan Najeriya a Shari MansurGwamnatin Neja na yunƙurin haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man feturJirgin sojoji ya kashe ƴan sa-kai a ƙoƙarin fatattakar ƴanbindiga'Hadarin mota ya yi sanadiyyar matasa 22 'yan asalin KanoGwamnatin Tinubu ta jefa ƴan Najeriya fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci - NLCSojoji sun ce sun hallaka ƴan ta'adda 60 a jihar BornoAn kama mutane 41 kan zargin kashe DPO a Kano
X whatsapp