• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta
  • General

Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta

By
'ƴan Bindiga
-
August 29, 2024
Arewa Award

Rundunar Tsaron Najeriya ta ce sojojinta sun kashe ‘ƴan bindiga sama da 1,000 a cikin wannan watan a faɗin Najeriya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Rundunar Tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba, inda a ciki ya bayyana cewa aikace-aikacen sojin yana matuƙar daƙile ayyukan ƙungiyoyin ƴan bindigar.

“Muna sane cewa muna yaƙi ne da maƙiya marasa imani, wanda hakan ya sa dole mu ƙara ƙaimi wajen dakatar da su.”

Ya ce daga shirye-shiryen sojojin, akwai takura ƴan bindigar domin hana su sakat, “sannan sojojin suna bibiyar kwamandojin ƴan ta’addan da yaransu da ma masu taimaka musu.”

Ya ƙara da cewa tuni sun ga bayan wasu manyan kwamandojin ƙungiyoyin a watan “A Arewa ta Gabas an kashe irin Munir Arika da Sani Dilla (AKA Dan Hausawan Jibilarram) da Ameer Modu da Dan Fulani da Fari Fari da Bakoura Araina Chikin da Dungusu da Abu Darda da Abu Rijab.”

Read Also:

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a yankin Arewa maso Yamma sojojin sun ga bayan manyan ƴan bindiga kamar su Kachalla Ɗan Ali Garin Fadama da Kachalla Ɗan Mani Na Inna da Kachalla Basiru Zakariyya da Sani Baka Tsine da Inusa Zangon Kuzi da Ibrahim da Tukur da Kamilu Buzaru da sauransu.

“Sojoji sun samu gagarumar nasara a kan ƴan bindigar, sannan kuma suna ci gaba da ƙara ƙaimi a aikace-aikacen da suke yi a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas domin magance matsalar tsaron da ake fama da su.”

Ya ce jimilla a watan Agusta, sojoji sun kashe ƴan ta’adda 1166, an kama guda 1,096 sannan an tseratar da waɗanda aka kama guda 721.

Haka kuma a cewar sanarwar, ak ƙwato makamai 391, da alburusai 15,234, sannan sun daƙile satar mai da aka ƙiyasta ya kai na Naira biliyan 5.

“Aikace-aikacen sojojin sun sa ƴan bindigar sun ja baya sosai, wanda hakan ya sa suke ta miƙa wuya, musamman a Arewa maso Gabas,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa sojojin za su ƙara matsa lamba a sauran yankunan domin samun irin wannan nasarar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Agusta
  • Edward Buba
Previous articleSojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna
Next articleGwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki
'ƴan Bindiga

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna

‘Ƴan Najeriya miliyan 30 za su fuskanci matsalar yunwa a 2026’

Mun Karbi korafin cin zarafin Mata sama da dubu 3 cikin shekara daya a jihar Kano – NHRC

Shugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna – Kotun Ƙoli

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

KAROTA ta bukaci Al’ummar jihar Kano su bawa jami’anta hadin kai

Gwamnatin Neja ta ɗora alhakin sace ɗalibai kan makarantar

Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

SAEMA 2025: IMPR Ta kaddamar da Littafi Kan Yaki da Sha da fatauci miyagun ƙwayoyi da fasa kwauri

Recent Posts

  • Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a Kaduna
  • Ba a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya – Sanata Ningi
  • An ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin Nijar
  • Turkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar Tsaro
  • Najeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasar

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1687 days 16 hours 28 minutes 41 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1669 days 18 hours 10 minutes 6 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Sojoji sun lalata maɓoyar masu sace mutane tare da ceto wasu a KadunaBa a nemi izinin majalisa ba kafin kai harin Amurka a Najeriya - Sanata NingiAn ji harbe-harbe da fashe-fashe a kusa babban filin jirgin NijarTurkiyya za ta tallafawa Nijeriya ta yaki matsalar TsaroNajeriya da Turkiyya za su ƙarfafa alaƙa a ziyarar da Tinubu ke yi a ƙasarkaro na biyu a shekarar 2026 Babban layin wutar lantarkin Najeriya ya sake lalacewaMatatar man Ɗangote ta ƙara farashin man fetur da naira 100Shalkwatar tsaron Najeriya ta tabbatar da yunƙurin juyin mulki a watan Oktoban baraAna tsammanin haifar jarirai dubu 700 cikin shekarar 2026 a Kano - GwamnatiJOHESU - Gwamnatin tarayya ce ta janyo yajin aikin ma'aikatan asibitiGwamnan Kano zai koma Jam'iyyar APCGwamnan Kano ya nada sabon mai ba shi shawara kan SiyasaJam’iyyar NNPP ya yi martani kan fitar Gwamnan Kano daga NNPPGwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya fice daga Jam'iyyar NNPPAmurka na son Najeriya ta ƙara jajircewa wajen kare Kiristoci
X whatsapp