• Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Search
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Sign in
Welcome! Log into your account
Forgot your password? Get help
Password recovery
Recover your password
A password will be e-mailed to you.
PRNIGERIA PRNigeria Hausa
PRNIGERIA PRNIGERIA
  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
Home General Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta
  • General

Yadda Sojojin Najeriya suka kashe ƴanbindiga sama da 1,000 a Agusta

By
'ƴan Bindiga
-
August 29, 2024
Arewa Award

Rundunar Tsaron Najeriya ta ce sojojinta sun kashe ‘ƴan bindiga sama da 1,000 a cikin wannan watan a faɗin Najeriya.

Wannan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa da Daraktan Rundunar Tsaron Najeriya, Manjo Janar Edward Buba, inda a ciki ya bayyana cewa aikace-aikacen sojin yana matuƙar daƙile ayyukan ƙungiyoyin ƴan bindigar.

“Muna sane cewa muna yaƙi ne da maƙiya marasa imani, wanda hakan ya sa dole mu ƙara ƙaimi wajen dakatar da su.”

Ya ce daga shirye-shiryen sojojin, akwai takura ƴan bindigar domin hana su sakat, “sannan sojojin suna bibiyar kwamandojin ƴan ta’addan da yaransu da ma masu taimaka musu.”

Ya ƙara da cewa tuni sun ga bayan wasu manyan kwamandojin ƙungiyoyin a watan “A Arewa ta Gabas an kashe irin Munir Arika da Sani Dilla (AKA Dan Hausawan Jibilarram) da Ameer Modu da Dan Fulani da Fari Fari da Bakoura Araina Chikin da Dungusu da Abu Darda da Abu Rijab.”

Read Also:

  • Dangote ya kai ƙarar tsohon shugaban NMDPRA zuwa EFCC
  • APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara
  • Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera

Sanarwar ta kuma ƙara da cewa a yankin Arewa maso Yamma sojojin sun ga bayan manyan ƴan bindiga kamar su Kachalla Ɗan Ali Garin Fadama da Kachalla Ɗan Mani Na Inna da Kachalla Basiru Zakariyya da Sani Baka Tsine da Inusa Zangon Kuzi da Ibrahim da Tukur da Kamilu Buzaru da sauransu.

“Sojoji sun samu gagarumar nasara a kan ƴan bindigar, sannan kuma suna ci gaba da ƙara ƙaimi a aikace-aikacen da suke yi a yankunan Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya da Kudu maso Kudu da Kudu maso Gabas domin magance matsalar tsaron da ake fama da su.”

Ya ce jimilla a watan Agusta, sojoji sun kashe ƴan ta’adda 1166, an kama guda 1,096 sannan an tseratar da waɗanda aka kama guda 721.

Haka kuma a cewar sanarwar, ak ƙwato makamai 391, da alburusai 15,234, sannan sun daƙile satar mai da aka ƙiyasta ya kai na Naira biliyan 5.

“Aikace-aikacen sojojin sun sa ƴan bindigar sun ja baya sosai, wanda hakan ya sa suke ta miƙa wuya, musamman a Arewa maso Gabas,” in ji shi, sannan ya ƙara da cewa sojojin za su ƙara matsa lamba a sauran yankunan domin samun irin wannan nasarar.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
  • TAGS
  • Agusta
  • Edward Buba
Previous articleSojoji sun hallaka ‘Yan Ta’adda 8 a jihar Kaduna
Next articleGwamnatin Najeriya ta bai wa ƴan kasuwa wa’adin rage farashin kayayyaki
'ƴan Bindiga

RELATED ARTICLESMORE FROM AUTHOR

Shugaban Najeriya zai iya dakatar da gwamna – Kotun Ƙoli

NNPC ya fara bincike kan fashewar bututun mai a jihar Delta

Har yanzu sojojin Najeriya 11 na Burkina Faso – Tugga

Kwankwaso ya ce matsalar tsaro na neman fin karfin Gwamnatin Nijeriya

NDLEA ta cafke miyagun ƙwayoyi da darajarsu ta haura naira biliyan 6

KAROTA ta bukaci Al’ummar jihar Kano su bawa jami’anta hadin kai

Gwamnatin Neja ta ɗora alhakin sace ɗalibai kan makarantar

Kotu ta yanke wa Nnamdi Kanu hukuncin daurin rai da rai

SAEMA 2025: IMPR Ta kaddamar da Littafi Kan Yaki da Sha da fatauci miyagun ƙwayoyi da fasa kwauri

Gwamnatin Najeriya ta dakatar da fara karɓar harajin man fetur

Majalisar Dattawan Najeriya ta tabbatar da Amupitan a matsayin shugaban INEC

NAHCON ta bayyana dalilian da suka saka Saudiya rage mata kujerun aikin hajji bana

Recent Posts

  • Dangote ya kai ƙarar tsohon shugaban NMDPRA zuwa EFCC
  • APC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna Fubara
  • Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera
  • ICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsa
  • Ku daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1667 days 11 hours 12 minutes 47 seconds,



Baptist School Students, Kaduna
1649 days 12 hours 54 minutes 12 seconds

Report By: prnigeria.com/hausa

Book on Sales: Boko Haram Media War: An Encounter with the Spymaster

boko haram

Click Here:To Order Now!

  • Gida
  • DUNIYA
  • Labarai
  • SIYASA
  • TARIHI
  • Taska
  • WASANNI
© 2020 PRNigeria. All Rights Reserved.
Latest News
Dangote ya kai ƙarar tsohon shugaban NMDPRA zuwa EFCCAPC ta yi watsi da yunƙurin tsige Gwamna FubaraMadugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar TouaderaICPC za ta ci gaba da binciken shugaban NMDPRA duk da Dangote ya janye ƙorafinsaKu daina kirana da na janye takarar shugabancin kasa a shekarar 2027Ƴansanda sun ɗauke makeken bam ɗin da aka gani a jihar NejaSojojin Najeriya sun kashe ƴanbindiga tare da ceto wasu da aka sace a BornoNan gaba za ku ga Amfanin dokar haraji -TinubuAmurka ta fara kai harin soji Arewacin NijeriyaSojoji sun daƙile yunƙurin harin ƴanbidiga a BornoGwamnatin Nijeriya ta yi watsi da kudirin hukuncin kisa ga masu garkuwaADC ta buƙaci a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar harajiGwamnati Nijeriya ta haramta fitar da itace zuwa ƙasashen wajeTinubu ya maye gurbin Engr Farouk daga shugabancin hukumar NMDPRAICPC ta ce zata binciki shugaban hukumar NMDPRA
X whatsapp