Home AFIRKA Sojojin Mali sun ce sun magance harin da aka kai Bamako

Sojojin Mali sun ce sun magance harin da aka kai Bamako

Gwamnatin mulkin sojin Mali ta ce ta yi nasarar daƙile wani harin ta’addanci a babban birnin ƙasar, tana mai cewa yanzu hankula sun kwanta.

Rundunar sojin ƙasar tana gudanar da aikin tabbatar da tsaro bayan fafatawar da ta yi da ƴan bindigar da suka ƙaddamar da farmaki kan wata Cibiyar Ƴan sanda a Bamako.

A sanyin safiyar wannan Talatar ce, ƴan bindigar suka kai farmakin a kusa da filin jiragen sama kamar yadda wasu da suka shaida lamarin suka bayyana, inda suka tabbatar cewa, lallai sun ji ƙarar harbe-harbe da fashe-fashen bama-bamai.

Kamfanin Dillancin Labarai na AFP ya rawaito cewa, an kulle filin jiragen saman na wani  ɗan lokaci sakamakon fargabar abin da ka iya faruwa.

Tuni rundunar sojin ƙasar ta buƙaci mazauna yankin da su yi ƙaura na wucen-gadi kafin fitar da wata sabuwar sanarwa nan gaba.

Tun bayan juyin mulkin 2021, gwamnatin mulkin sojin Mali ke yaƙi da ƙungiyoyin ƴan ta’adda da suka haɗa da ƴan aware da mayaƙan jihadi masu alaka da al-Qaeda da ISIL.

A ƙarƙashin jagorancin shugaban mulkin sojin Mali, Kanar Assimi Goita, ƙasar ta yanke hulɗa da aminanta na ƙasashen Turai da kuma tsohuwar uwargijiyarta, Faransa, inda ta karkata hankalinta kan kulla alaƙa da Rasha da sojojin haya na Wagner domin samun agaji a fannin yaƙi da ƴan ta’adda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
COAS Ya Bukaci Bojojin Nijeriya da su Mayar da Hankali Wajen Kare Rayukan Fararen HulaTURA TA KAI BANGO: Bayan Mutuwar Bashar Sani, Dole ne Arewa Ta Fuskanci MatsalolintaDangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige Fubara
X whatsapp