Home AFIRKA Fasinja 78 sun mutu bayan nutsewar jirgin ruwan da suke ciki a...

Fasinja 78 sun mutu bayan nutsewar jirgin ruwan da suke ciki a Congo

Aƙalla mutane 78 ake fargabar sun rasa rayukansu a Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Congo bayan nutsewar wani jirgin ruwa yayin da yake ƙoƙarin ketara tabkin Kivu ɗauke da fasinjoji 278.

Gwamnan Lardin Kudancin Kivu da ke gabashin Jamhuriyar Congon Jean Jacques ne ya tabbatar da adadin mamatan na mutane 78, da kuma yawan fasinjojin kusan 300 da ke cikin jirgin da ya nutse.

Sai dai ya ce basu kammala tantance adadin rayukan da suka salwanta a haɗarin ba, aikin da ya ce zai ɗauki jami’an ceto aƙalla kwanaki uku suna yi.

Har zuwa daren jiya dai an riƙa samun bayanai masu cin karo da juna akan yawan waɗanda haɗarin jirgin ruwan ya rutsa da su, domin a yayin da mahukuntan lardin Kivu suka bayar da nasu alƙaluman, takwarorinsu na arewacin Lardin Kivun cewa suka yi mutane 28 suka rasa rayukansu, yayin da wasu 58 suka tsira.

Ɗaukar fasinjoji fiye da kima ke kan gaba a cikin dalilan dake haddasa yawaitar nutsewar jiragen ruwa a Jamhuriyar Congo, lamarin da ake kyautata zaton ko a wannan karon shi ne musababbin haɗarin da ya auku.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp