Home AFIRKA Rashawa na janyo wa Uganda asarar sama da dala biliyan 2 duk...

Rashawa na janyo wa Uganda asarar sama da dala biliyan 2 duk shekara

Uganda na yin asarar kuɗin da ya kai Dalar Amurka biliyan 2 da miliyan 500 a duk shekara saboda cin hancin, kwatankwacin kaso 1 bisa 4 na kasafin kuɗin da ƙasar ke yi, kamar yadda hukumar da ke yaƙar cin hanci a  ƙasar ta tabbatar.

A cewar shugabar hukumar yaƙi da cin hanci ta Uganda Beti Kamya Turwomwe, ƙasar na asarar sama da tiriliyan 9 da miliyan 100 na kuɗin ƙasar Shiling, kwatankwacin dala biliyan 2 da miliyan 500 a duk shekara.

Ta ce wannan ya kai kaso 23 cikin 100 na kasafin kuɗin ƙasar, abin da ke zama wani babban ƙalubale ga ayyukan daƙile cin hanci a ƙasar.

Cin hanci da rashawa wata gagarumar matsala ce da ke addabar gabashin Afirka.

Shugaban ƙasar Uganda Yoweri Musaveni ya sha nanata alwashin ɗaukar matakan da za su kawo ƙarshen matsalar cin hanci ganin yadda matsalar ta ratsa cikin jami’an gwamnati.

Turwomwe ta ce sashin da ta ke jagoranta ya samu nasrar ƙwato dala miliyan 2 da aka wawushe, inda ta nuna damuwa kan rashin sanya kuɗi a hukumar da take jagoranta.

Wannan kalaman nata ya biyo bayan rahoton shekara-shekara da ake fitarwa na cibiyar bincike kan tabbbatar da ganin an yi ayyukan gwamnati a buɗe babu kumbiya-kumbiya.

Rahoton na zuwa mako guda da shugaban Uganda Yoweri Musaveni ya sanar da yafewa wasu manyan jami’an gwamnati da aka ɗaue shekara 10 saboda kamasu da badaƙalar dala miliyan 1 da miliyan 200.

Musaveni ya yafe musu bayan sun kammala shekara 5 a gidan 5, abinda ya tunzura kungiyoyin fararan hula

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp