Home AFIRKA Shugabannin ƙasashen Benin da Senegal sun gana don farfaɗo da alaƙarsu

Shugabannin ƙasashen Benin da Senegal sun gana don farfaɗo da alaƙarsu

Shugaban ƙasar Senegal Bassirou Diomaye Faye ya kai wata ziyarar aiki na yini guda ƙasar Benin da yammacin jiya Talata, da nufin ƙarfafa dangantaka da farfaɗo da haɗin gwiwa tsakanin Benin da Senegal.

Shugaba Patrice Talon ya nuna farin cikinsa da wannan ziyarar, musamman da tazo kwanaki kaɗan gabanin bikin tunawa da ranar ƴancin ƙan ƙasar.

Anasa ɓangaren Bassirou Diomaye Faye ya bayyana goyon bayan ƙasarsa ga yaƙin da Benin ke yi da ƴan ta’adda, tare da fatan ƙasashen biyu za su samu ci gaba mai ɗorewa a fannin kasuwanci.

Dangane da Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afrika ECOWAS kuwa, Faye ya tunanar da shugaba Talon irin ƙalubalen da ƙungiyar ke fuskanta, acewarsa dole ne kamar UEMOA, sai an kawo sauye – sauye domin tunkarar halin da ake ciki yanzu haka.

Wannan dai ita ce ziyarar farko da wani shugaban ƙasar Senegal ya kai Cotonou tun bayan da Patrice Talon ya hau kan karagar mulki a shekarar 2016.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp