Home General Likitocin Nijeriya sun fasa Yajin Aiki

Likitocin Nijeriya sun fasa Yajin Aiki

Ƙungiya Likitoci Masu Neman Ƙwarewa ta Najeriya ta soke yajin aikin da ta shirya gudanarwa a faɗin ƙasar.

Matakin na zuwa ne bayan ganawar da kwamitin zartarwa na ƙungiyar ya gudanar a birnin Uyo na jihar Akwa Ibom, inda ƙungiyar ta sake duba batun.

A cikin watan Janairu ne dai ƙungiyar ta yi barazanar tafiya yajin aiki a fadin ƙasar saboda kasa biya mata buƙatunta da gwamnati ta yi.

Likitocin dai na buƙatar a sake duba tare da inganta kuɗaɗen alawus ɗin horaswa da ake ba su, yayin da suke kuka da rashin biyansu wasu alawus-alawus, da rashin biyan wasu daga cikin mambobinsu da sabon tsarin albashi da ƙasar ta amince da shi.

Rahotonni sun ce a ƙarshen ganawar majalisar zartarwar ƙungiyar, likitocin sun yaba wa gwamnatin tarayya game da sakin sabuwar sanarwar biyan kuɗaɗen alawus-alawus na horaswa ga likitocin.

Haka kuma likitocin sun nemi gwamnatin tarayyar da ta biya wasu daga cikin mambobinta da ke bin gwamnatin bashin kuɗaden alawus-alawus.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp