Home AFIRKA Faye ya ƙaddamar da shiri mai dogon zango dan ciyar da Senegal...

Faye ya ƙaddamar da shiri mai dogon zango dan ciyar da Senegal gaba

Gwamnatin Senegal ta ƙaddamar da shirinta mai nisan zango na ciyar da ƙasar gaba, wanda take fatan za a kammala aiwatar da shi cikin shekaru 25 masu zuwa.

Sai dai gwamnatin Senegal ɗin ta bayyana wasu daga cikin muradun da tsara cim-musu cikin shekaru 5.

Muhimman muradun da take fatan cim-musu a gejeren zango kuwa, sun haɗa da rage nauyin bashin da ke kan ƙasar daga kaso 83.7 zuwa kaso 70 cikin 100.

Sai kuma rage giɓin kasafin kuɗi zuwa kashi 3 nan gaba kaɗan, saɓanin giɓin kashi 10.4 da ƙididdiga ta nuna cewar gwa,natin senegal din ta yi fama da shi daga shekarar 2019 zuwa 2023.

Ƙalubale na gaba da gwamnatin Senegal ta sha alwashin magancewa shi ne matsin rayuwa, inda ta yi alƙawarin cikin shekaru biyar da ke tafe, za ta ƙara yawan matsakaicin albashin da ‘yan ƙasar ke samu da kashi 50 cikin 100, kwatankwacin ƙarin daga dala dubu 1, 660 zuwa aƙalla dala dubu 2,648, yayin da kuma za a rage hauhawar farashin kayayyaki zuwa kashi 2 cikin shekaru 5.

Shugaban Senegal Basirou Diomaye Faye da Fira Ministansa Ousmane Sonko ne suka jagoranci kaddamar da gagarumin shirin a garin Diamniadio, mai nisan kilomita 30 daga Dakar babban birnin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp