Aƙalla mutum 13 ne suka mutu a wani hari da da ake zargin dakarun RSF ne suka kai a kudancin birnin Khartoum na ƙasar Sudan.
Read Also:
An yi zargin cewa mayaƙan ƙungiyar sun buɗe wuta kan fararen hula a garin Al Hilaliya da ke jihar Al Jazeera, da ke kudancin Khartoum.
An samu rahotonnin sace kayyaki da cinna wa gidaje wuta. An dai ɗauki fiye da shekara guda ana gwambza yaƙi tsakanin RSF da sojojin ƙasar.
Yaƙin ya jefa ƙasar cikin mawuyacin halin buƙatar jin ƙai, yayin da fiye da mutum miliyan 11 suka rasa muhallansu.