Home AFIRKA Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera

Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera


Madugun adawa na jamhuriyyar Afrika ta tsakiya, Anicet-George Dologuele yayi watsi da sakamakon zaɓen ƙasar da ke bayyana shugaba Faustin-Archange Touadera a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen watan jiya.

Tun gabanin sakamako Touadera mai shekaru 68 shi ne aka yiwa tsammanin ya lashe zaɓen yayinda sakamako ya nuna shi a matsayin wanda ya samu fiye da kashi 76 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa.

Nasarar kai tsaye ta baiwa Touadera damar ci gaba da mulki a wa’adi na 3, bayan da tun a watan Oktoban bara ya sanar da aniyar sake tsayawa takara lamarin da ƴan adawa ke yiwa kallo a matsayin wani yunƙurin ci gaba da mulkin kama karya a ƙasar.

Sai dai madugun adawar Dologuele wanda ya samu kashi 15 na yawan ƙuri’un da aka ƙada a zaɓen da ya bashi damar zuwa na biyu ya ce an tafka maguɗi ne a zaɓen tare da sauya sakamako.

A cewar Dologuele ba a baiwa jama’a sakamakon abin da suka zaɓa ba, ta yadda hukumar zaɓe ta yi zuraren ƙuri’u a wasu wuraren don nuna shugaban a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Shugaba Faustin-Archange Touadera wanda ke samun cikakken goyon bayan Rasha da ta tallafa masa wajen kawo ƙarshen yaƙin da ƙasar ke fuskanta kai tsaye nasarar ta bashi damar ci gaba da jan ragamar ƙasa har zuwa ƙarin shekaru 5 a wa’adi na 3.

Ana kallon nasarar da ya yi ta kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe a jamhuriyyar Afrikan ta tsakiya ya taimaka masa matuƙa wajen samun cikakken goyon bayan jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp