Shugaba Faye ya rushe majalisar dokokin Senegal tare da sanya ranar sake zaɓe

Shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye ya rushe majalisar dokokin ƙasar da ƴan adawa ke da rinjaye a cikinta, tare da sanar da ranar 17 ga watan Nuwamba don gudanar da zaɓensu.

Faye wanda ya lashe zaɓen ƙasar da aka gudanar a watan Maris na wannan shekarar, tare da faraministansa Ousmane Sonko, sun yi wa ƴan ƙasar alkawarin kawo sauyi mai ma’ana.

To sai dai gwamnatin su na fuskantar koma baya wajen aiwatar da manufofinta, sakamakon rashin rinjayen da su ke da shi a zauren majalisar.

A cewar kundin tsarin mulkin Senegal, Faye na da ikon rushe majalisar dokokin da ke da rinjayen ƴan adawa, tare da sanya ranar da za a gudanar da zaɓensu don samun rinjayen da suke buƙata, wanda hakan kuma zai basu damar aiwatar da kudurorinsu.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 28 minutes 43 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 10 minutes 8 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com