Home AFIRKA Shugaba Faye ya rushe majalisar dokokin Senegal tare da sanya ranar sake...

Shugaba Faye ya rushe majalisar dokokin Senegal tare da sanya ranar sake zaɓe

Shugaban Senegal Bassirou Diomaye Faye ya rushe majalisar dokokin ƙasar da ƴan adawa ke da rinjaye a cikinta, tare da sanar da ranar 17 ga watan Nuwamba don gudanar da zaɓensu.

Faye wanda ya lashe zaɓen ƙasar da aka gudanar a watan Maris na wannan shekarar, tare da faraministansa Ousmane Sonko, sun yi wa ƴan ƙasar alkawarin kawo sauyi mai ma’ana.

To sai dai gwamnatin su na fuskantar koma baya wajen aiwatar da manufofinta, sakamakon rashin rinjayen da su ke da shi a zauren majalisar.

A cewar kundin tsarin mulkin Senegal, Faye na da ikon rushe majalisar dokokin da ke da rinjayen ƴan adawa, tare da sanya ranar da za a gudanar da zaɓensu don samun rinjayen da suke buƙata, wanda hakan kuma zai basu damar aiwatar da kudurorinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp