Tsohon shugaban majalisar wakilai, Yakubu Dogara, ya ce koma-baya da ake samu a yankin Arewa laifi ne na jagororin siyasar yankin.
Ya kuma yi kira ga ƴan Najeriya da su goya wa Tinubu baya kan yunƙurinsa na inganta tattalin arzikin ƙasar ta hanyar ƙudurorin haraji.
Read Also:
- Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara Ne
- Pantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama’a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a Gombe
- Ma’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’
Dogara ya bayyana hakan ne a wani taron jagororin kiristoci ƴan arewacin Najeriya, inda ya ce jagororin yankin ba su yi amfani da damar da suka ba na kusan shekara 40, wanda hakan a cewarsa ya jefa yankin talauci da rashin aikin yi.
“Ba Tinubu ko yankin kudu ba ne matsalarmu. Wasu na ƙorafin cewa Yarbawa suna samun muƙamai da yawa, amma kar mu manta, mun yi mulkin sama da shekara 40. Me za mu nuna? har yanzu arewa na nan yadda take,” in ji shi, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.












