Home AFIRKA ECOWAS ta caccaki hare-haren ta’addanci da aka kai babban birnin Mali

ECOWAS ta caccaki hare-haren ta’addanci da aka kai babban birnin Mali

Ƙungiyar ƙasashen yammmacin nahiyar Afrika,  ECOWAS ta caccaki hare-haren da ƴan ta’adda su ka kai babban birnin Mali, Bamako a ranar Talata.

A wata sanarwa, ECOWAS ta bayyana rashin jin  daɗin ta a game da waɗannan hare-hare, waɗanda ta ce su na barazana ga zamn lafiyar yankin yammacin nahiyar  Afrika.

Sanarwar ta kara da cewa Kungiyar ta na jaddada ƙudirinta a kan duk wani shiri da kawo zaman lafiya mai ɗorewa a yankin.

A ranar Talata ce aka kai wa birnin Bamako munanan hare-hare, waɗanda ƙungiyyar nan mai ikirarin jihadi da ke da alaƙa da Al-Qaeda ta ɗauki alhakin kaiwa. Har yanzu dai  ba a bayyana adadin mutanen da waɗannan hare-hare su ka rutsa da su ba.

Birnin Bamako bai cika fuskantar hare-hare na masu ikirarin jihadi ba kamar yadda wasu sassan kasarke fuskanta kusan kullayaumin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp