Home AFIRKA Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera

Madugun adawar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya ya ƙalubalanci nasarar Touadera


Madugun adawa na jamhuriyyar Afrika ta tsakiya, Anicet-George Dologuele yayi watsi da sakamakon zaɓen ƙasar da ke bayyana shugaba Faustin-Archange Touadera a matsayin wanda ya yi nasara a zaɓen watan jiya.

Tun gabanin sakamako Touadera mai shekaru 68 shi ne aka yiwa tsammanin ya lashe zaɓen yayinda sakamako ya nuna shi a matsayin wanda ya samu fiye da kashi 76 na yawan ƙuri’un da aka kaɗa.

Nasarar kai tsaye ta baiwa Touadera damar ci gaba da mulki a wa’adi na 3, bayan da tun a watan Oktoban bara ya sanar da aniyar sake tsayawa takara lamarin da ƴan adawa ke yiwa kallo a matsayin wani yunƙurin ci gaba da mulkin kama karya a ƙasar.

Sai dai madugun adawar Dologuele wanda ya samu kashi 15 na yawan ƙuri’un da aka ƙada a zaɓen da ya bashi damar zuwa na biyu ya ce an tafka maguɗi ne a zaɓen tare da sauya sakamako.

A cewar Dologuele ba a baiwa jama’a sakamakon abin da suka zaɓa ba, ta yadda hukumar zaɓe ta yi zuraren ƙuri’u a wasu wuraren don nuna shugaban a matsayin wanda ya lashe zaɓen.

Shugaba Faustin-Archange Touadera wanda ke samun cikakken goyon bayan Rasha da ta tallafa masa wajen kawo ƙarshen yaƙin da ƙasar ke fuskanta kai tsaye nasarar ta bashi damar ci gaba da jan ragamar ƙasa har zuwa ƙarin shekaru 5 a wa’adi na 3.

Ana kallon nasarar da ya yi ta kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe a jamhuriyyar Afrikan ta tsakiya ya taimaka masa matuƙa wajen samun cikakken goyon bayan jama’a.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp